fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe ‘Yan Sanda uku a Anambra

Date:

Wasu ‘yan bindiga da har yanzu ba a tantance ko su waye ba sun kashe jami’an ‘yan sanda uku a ranar Alhamis da yamma a jihar Anambra.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a unguwar Umunze da ke karamar hukumar Orumba ta Kudu a jihar.

An kuma tattaro cewa jami’an da aka kashe ‘yan sandan wayar tafi da gidanka ne da ke tare da 29 PMF da 54 PMF Umunze.

Da yake tabbatar da harin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Anambra, Mista Tochukwu Ikenga, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici.

Kakakin ‘yan sandan ya kara da cewa yana daga cikin mafi girman farashin da jami’an tsaro ke biya wajen yi wa kasa hidima amma rundunar ‘yan sandan ba ta hana su ci gaba ba.

Ya ce tuni rundunar hadin gwiwa ta shigo yankin, kuma ana ci gaba da farautar maharan yayin da aka tsaurara matakan tsaro na hadin gwiwa a yankin.

Wannan na zuwa ne mako guda bayan da rahotanni suka ce an kashe ‘yan sanda hudu a wani sabon hari da aka kai a wata jihar Imo da ke Kudu maso Gabashin kasar.

Haka kuma an kashe wasu fararen hula biyu a harin na Imo a mahadar Okpala da ke karamar hukumar Ngorokpala a jihar.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp