Kimanin ‘yan bindiga shida ne suka kai farmaki ofishin ‘yan sanda da ke karamar hukumar Adavi a jihar Kogi, inda suka kashe ‘yan sanda uku da ke bakin aiki.
Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan bindigar sun kai hari ofishin ‘yan sandan ne ta bangare daban-daban.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP William Aya, ya tabbatar da kai harin.