fidelitybank

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Date:

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga cikin jami’anta sakamakon hare-haren da wasu ƴan bindiga suka kai kan sansanonin soji da ke jahohin Neja da Kaduna.

Rundunar ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafin sada zumunta na X.

A cewar sanarwar, hare-haren sun faru ne a ranar Litinin, 24 ga Yuni, 2025, a sansanonin sojin da ke Kwanar Dutse Mairiga da Boka a Jihar Neja, da kuma Aungwan Turai da ke ƙaramar hukumar Chikun a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun ce ƴan bindigar sun kai hari ta ɓangarori uku a lokaci guda, lamarin da ya sa dakarun soji suka mayar da martani cikin gaggawa.

A yayin musayar wuta ne rundunar soji ta tura dakarun ƙasa da na sama don fatattakar maharan, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Rundunar ta ce an kashe ƴan bindiga da dama yayin gumurzun da ya ɗauki sa’o’i.

“Sai dai kuma, an kashe mana wasu jami’ai yayin musayar wuta da ƴan bindigar.”, in ji sanarwar.

Baya ga haka, rundunar ta kuma ce wasu sojoji huɗu sun jikkata sakamakon harbin bindiga kuma suna samun kulawar a asibiti.

Rundunar sojin ta bayyana waɗanda suka mutu a matsayin “jarumai” da suka tsaya tsayin daka wajen kare matsayinsu da mutuncin ƙasa.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp