fidelitybank

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Date:

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga cikin jami’anta sakamakon hare-haren da wasu ƴan bindiga suka kai kan sansanonin soji da ke jahohin Neja da Kaduna.

Rundunar ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafin sada zumunta na X.

A cewar sanarwar, hare-haren sun faru ne a ranar Litinin, 24 ga Yuni, 2025, a sansanonin sojin da ke Kwanar Dutse Mairiga da Boka a Jihar Neja, da kuma Aungwan Turai da ke ƙaramar hukumar Chikun a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun ce ƴan bindigar sun kai hari ta ɓangarori uku a lokaci guda, lamarin da ya sa dakarun soji suka mayar da martani cikin gaggawa.

A yayin musayar wuta ne rundunar soji ta tura dakarun ƙasa da na sama don fatattakar maharan, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Rundunar ta ce an kashe ƴan bindiga da dama yayin gumurzun da ya ɗauki sa’o’i.

“Sai dai kuma, an kashe mana wasu jami’ai yayin musayar wuta da ƴan bindigar.”, in ji sanarwar.

Baya ga haka, rundunar ta kuma ce wasu sojoji huɗu sun jikkata sakamakon harbin bindiga kuma suna samun kulawar a asibiti.

Rundunar sojin ta bayyana waɗanda suka mutu a matsayin “jarumai” da suka tsaya tsayin daka wajen kare matsayinsu da mutuncin ƙasa.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...
X whatsapp