fidelitybank

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Date:

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga cikin jami’anta sakamakon hare-haren da wasu ƴan bindiga suka kai kan sansanonin soji da ke jahohin Neja da Kaduna.

Rundunar ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafin sada zumunta na X.

A cewar sanarwar, hare-haren sun faru ne a ranar Litinin, 24 ga Yuni, 2025, a sansanonin sojin da ke Kwanar Dutse Mairiga da Boka a Jihar Neja, da kuma Aungwan Turai da ke ƙaramar hukumar Chikun a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun ce ƴan bindigar sun kai hari ta ɓangarori uku a lokaci guda, lamarin da ya sa dakarun soji suka mayar da martani cikin gaggawa.

A yayin musayar wuta ne rundunar soji ta tura dakarun ƙasa da na sama don fatattakar maharan, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Rundunar ta ce an kashe ƴan bindiga da dama yayin gumurzun da ya ɗauki sa’o’i.

“Sai dai kuma, an kashe mana wasu jami’ai yayin musayar wuta da ƴan bindigar.”, in ji sanarwar.

Baya ga haka, rundunar ta kuma ce wasu sojoji huɗu sun jikkata sakamakon harbin bindiga kuma suna samun kulawar a asibiti.

Rundunar sojin ta bayyana waɗanda suka mutu a matsayin “jarumai” da suka tsaya tsayin daka wajen kare matsayinsu da mutuncin ƙasa.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...

Hisba ta kama ‘yan Mata 62 da zargin aikata baɗala a Kano

Hukumar Hisbah ta kama mutane 62 kan zargin aikata...
X whatsapp