fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe sakataren jam’iyyar PDP a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun kashe wani Musa Ille, sakataren jam’iyyar PDP a karamar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara.

‘Yan bindigar sun harbe Musa har lahira a kofar gidansa da ke garin Tsafe a yammacin ranar Litinin.

Marigayi Musa Ille ya kasance dan siyasa mai kishin kasa wanda ya bada gudunmawa sosai wajen samun nasarar jam’iyyar a zaben 2023 wanda ya samar da Dauda Lawal a matsayin gwamnan jihar, inji rahoton TVC.

Lamarin dai na zuwa ne ‘yan makonni bayan da aka kashe jigon jam’iyyar PDP Shafiu Abubakar tare da wasu mutane biyu a karamar hukumar Maradun ta jihar.

Marigayi Shafiu Abubakar yana daya daga cikin masu neman kujerar shugaban karamar hukumar Tsafe a karkashin jam’iyyar PDP.

Karamar hukumar Tsafe dai na fuskantar koma bayan ayyukan ‘yan fashi da makami a ‘yan kwanakin nan, sai dai gwamnatin ta ce ba za ta bar komai ba don ganin an dawo da zaman lafiya a duk yankunan da ake fama da rikici a fadin jihar.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp