fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe sakataren jam’iyyar PDP a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun kashe wani Musa Ille, sakataren jam’iyyar PDP a karamar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara.

‘Yan bindigar sun harbe Musa har lahira a kofar gidansa da ke garin Tsafe a yammacin ranar Litinin.

Marigayi Musa Ille ya kasance dan siyasa mai kishin kasa wanda ya bada gudunmawa sosai wajen samun nasarar jam’iyyar a zaben 2023 wanda ya samar da Dauda Lawal a matsayin gwamnan jihar, inji rahoton TVC.

Lamarin dai na zuwa ne ‘yan makonni bayan da aka kashe jigon jam’iyyar PDP Shafiu Abubakar tare da wasu mutane biyu a karamar hukumar Maradun ta jihar.

Marigayi Shafiu Abubakar yana daya daga cikin masu neman kujerar shugaban karamar hukumar Tsafe a karkashin jam’iyyar PDP.

Karamar hukumar Tsafe dai na fuskantar koma bayan ayyukan ‘yan fashi da makami a ‘yan kwanakin nan, sai dai gwamnatin ta ce ba za ta bar komai ba don ganin an dawo da zaman lafiya a duk yankunan da ake fama da rikici a fadin jihar.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp