fidelitybank

‘Yan Bindiga sun kashe mutum 7 a Benue

Date:

Rahotanni sun bayyana cewa wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane bakwai a wasu kauyuka biyu na karamar hukumar Gwer ta yamma a jihar Benue.

Mazauna ƙauyen sun ce lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata a Tse Fela da ke Mbabuande da Tse Akyegh da ke yankin Ikaaghev.

Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa al’ummar yankin lamarin ya faru ne da misalin karfe 3:30 na rana, inda maharan suka afka wa gidaje da muggan makamai tare da kashe mutane da kuma raunata wasu.

Shugaban karamar hukumar Gwer West, Andrew Ayande, ya tabbatar da cewa an kashe mutane bakwai a harin da aka kai wa al’ummomin biyu.

Ayande ya ce ci harin ya tilasta wa mutanen ƙauyen barin garuruwan da suke tun daga ranar Talata zuwa Laraba.

Sai dai mai magana da yawun ‘yan sanda a jihar Benue, SP Catherine Anene, ta ce har yanzu ba ta samu wani rahoto kan lamarin ba.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp