fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe mutane sama da 10 a Zamfara

Date:

‘Yan bidiga sun kai hare-hare a garin Nasarawar Godel na yankin karamar hukumar Birnin Magaji a jihar Zamfara.

Wannan dai shi ne karo na farko da ‘yan bindigar ke kai hari wannan gari, kamar yadda wani mutumin yankin da ya buƙaci a sakaya sunansa ya shaida wa BBC.

”Muna cikin halin farbaga da tashin hankali, inda ta kai ga wasu ba sa iya kwana a gidajensu, abin da ya faru jiya baƙon al’amari mu dai wajenmu, saboda ba mu taɓa fuskantar irin wannan hari ba”, in ji mutumin.

Ya ce maharan sun auka wa garin cikin gungunsu ɗauke da muggan makamai, inda suka kashe aƙalla mutum bakwai, tare da kashe wasu mutum uku a ƙauyen Dillashe mai maƙwabtaka da garin.

Mutumin garin ya shaida wa BBC cewa maharan sun kuma yi garkuwa da mutum aƙalla 15.

Maharan sun kuma ƙona gidajen mutanen garin tare da farfasa shaguna da ƙwashe dukiyoyi masu tarin yawa.

BBC ta kuma tuntuɓi kakakanin rundunar ‘yansanda da ɓangaren gwamnatin jihar Zamfara game da wannan harin, sun kuma ce za su bincika su sake kiranmu, amma har ya zuwa yanzu ba mu daga gare su ba.

latest news in nigeria today 
2021 ripples

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp