fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe mutane 9 a Kaduna

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe manoma kusan tara a Unguwan Danko da ke kusa da kauyen Dogon Dawa a yankin Birnin Gwari a jihar Kaduna.

Rahotanni na cewa an kashe manoman ne da yammacin ranar Asabar a lokacin da suke aikin gonakinsu.

A cewar wata majiya, ‘yan bindigar sun tafi ne tare da wasu manoma uku zuwa inda ba a san inda suke ba.

Shima zababben dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Kakangi Yahaya Musa ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa duk wadanda aka kashe manoma ne, yayin da wadanda suka samu raunukan harbin bindiga a yayin harin an garzaya da su asibiti domin yi musu magani.

A cewarsa, “Eh an tabbatar min da ranar Lahadi cewa ‘yan bindiga sun kashe manoma tara a Unguwar Danko kusa da kauyen Dogon Dawa a ranar Asabar da yamma, wasu kuma suka samu raunuka.

Ya bayyana cewa wasu daga cikin mutanen kauyen sun samu raunuka a lokacin da suka fuskanci ‘yan bindigar.

DSP Mohammed Jalige, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ya yi alkawarin zai dawo da cikakken bayanin lamarin, yayin da gwamnatin jihar ba ta mayar da martani kan harin ba.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp