Wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane shida tare da sace dabbobin da dama a wasu kauyuka biyu a jihar Sokoto a wasu hare-hare da suka kai a daren Laraba da yammacin Alhamis.
Al’ummar da abin ya shafa dai sun hada da Kwargaba da ke Wurno da Gatawa a cikin kananan hukumomin Sabon Birni na jihar.
Sokoto da ke jihohin Arewa maso yammacin Najeriya na fama da matsalar tsaro musamman sace-sacen mutane da fashi da makami. Laifuka sun zama ruwan dare kuma ‘yan fashin sun zama kamar ba za a iya murkushe su ba. A cewar Premium Times.
Wurno da Sabon Birni na daga cikin yankunan Sakkwato ta Gabas da ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga.