fidelitybank

;Yan bindiga sun kashe mutane 41 a Katsina

Date:

Rundunar ‘yan sanda reshen Jihar Katsina, ta ce, ‘yan bindiga sun kashe mutum aƙalla 41 sakamakon kwanton ɓaunar da suka yi wa ‘yan banga a jihar.

Sanarwar da kakakin rundunar, SP Gambo Isah, ya fitar ta ce lamarin ya faru ne ranar Alhamis da dare lokacin da mayaƙan sa-kai suka tunkari ‘yan bindigar da zimmar ƙwato dabbobinsu da ɓarayin shanu suka sace.

Sai dai mazauna yankin na cewa adadin ya zarta hakan, inda wasu ke cewa an kashe mutum kusan 60.

Karanta Wannan: ‘Yan bindiga sun harbe alkali a kotun Imo

“A ranar Laraba da misalin ƙarfe 10:00 na dare, ‘yan ta’adda sun kai hari gidan wani mutum mai suna Alhaji Muntari da ke Unguwar Audu Gare a Kandarawa na ƙaramar Hukumar Bakori, inda suka sace shanu 50 da awaki 30,” in ji sanarwar.

“Daga baya a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 10:00 na dare, ‘yan sa-kai da aka haramta suka taru daga ƙauyuka 11 na Bakori kuma suka nufi ‘yan ta’addan don ƙwato dabbobin da aka sace. Sun bi sawunsu har zuwa dajin Yargoje.

“Abin takaici, sai ‘yan ta’addan suka shirya musu kwanton-ɓauna, suka kashe 41 daga cikinsu sannan suka raunata biyu.”

SP Gambo ya ƙara da cewa kwamandan rundunar na Malumfashi ne ya jagoranci tawagar ‘yan sandan da suka kwaso gawar mamatan, yana mai cewa yanzu haka samamen haɗin gwiwa na jami’an na gudana “don gano waɗanda suka aikata kisan”.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp