fidelitybank

;Yan bindiga sun kashe mutane 41 a Katsina

Date:

Rundunar ‘yan sanda reshen Jihar Katsina, ta ce, ‘yan bindiga sun kashe mutum aƙalla 41 sakamakon kwanton ɓaunar da suka yi wa ‘yan banga a jihar.

Sanarwar da kakakin rundunar, SP Gambo Isah, ya fitar ta ce lamarin ya faru ne ranar Alhamis da dare lokacin da mayaƙan sa-kai suka tunkari ‘yan bindigar da zimmar ƙwato dabbobinsu da ɓarayin shanu suka sace.

Sai dai mazauna yankin na cewa adadin ya zarta hakan, inda wasu ke cewa an kashe mutum kusan 60.

Karanta Wannan: ‘Yan bindiga sun harbe alkali a kotun Imo

“A ranar Laraba da misalin ƙarfe 10:00 na dare, ‘yan ta’adda sun kai hari gidan wani mutum mai suna Alhaji Muntari da ke Unguwar Audu Gare a Kandarawa na ƙaramar Hukumar Bakori, inda suka sace shanu 50 da awaki 30,” in ji sanarwar.

“Daga baya a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 10:00 na dare, ‘yan sa-kai da aka haramta suka taru daga ƙauyuka 11 na Bakori kuma suka nufi ‘yan ta’addan don ƙwato dabbobin da aka sace. Sun bi sawunsu har zuwa dajin Yargoje.

“Abin takaici, sai ‘yan ta’addan suka shirya musu kwanton-ɓauna, suka kashe 41 daga cikinsu sannan suka raunata biyu.”

SP Gambo ya ƙara da cewa kwamandan rundunar na Malumfashi ne ya jagoranci tawagar ‘yan sandan da suka kwaso gawar mamatan, yana mai cewa yanzu haka samamen haɗin gwiwa na jami’an na gudana “don gano waɗanda suka aikata kisan”.

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp