Rundunar ‘yan sanda reshen Jihar Katsina, ta ce, ‘yan bindiga sun kashe mutum aƙalla 41 sakamakon kwanton ɓaunar da suka yi wa ‘yan banga a jihar.
Sanarwar da kakakin rundunar, SP Gambo Isah, ya fitar ta ce lamarin ya faru ne ranar Alhamis da dare lokacin da mayaƙan sa-kai suka tunkari ‘yan bindigar da zimmar ƙwato dabbobinsu da ɓarayin shanu suka sace.
Sai dai mazauna yankin na cewa adadin ya zarta hakan, inda wasu ke cewa an kashe mutum kusan 60.
Karanta Wannan: ‘Yan bindiga sun harbe alkali a kotun Imo
“A ranar Laraba da misalin ƙarfe 10:00 na dare, ‘yan ta’adda sun kai hari gidan wani mutum mai suna Alhaji Muntari da ke Unguwar Audu Gare a Kandarawa na ƙaramar Hukumar Bakori, inda suka sace shanu 50 da awaki 30,” in ji sanarwar.
“Daga baya a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 10:00 na dare, ‘yan sa-kai da aka haramta suka taru daga ƙauyuka 11 na Bakori kuma suka nufi ‘yan ta’addan don ƙwato dabbobin da aka sace. Sun bi sawunsu har zuwa dajin Yargoje.
“Abin takaici, sai ‘yan ta’addan suka shirya musu kwanton-ɓauna, suka kashe 41 daga cikinsu sannan suka raunata biyu.”
SP Gambo ya ƙara da cewa kwamandan rundunar na Malumfashi ne ya jagoranci tawagar ‘yan sandan da suka kwaso gawar mamatan, yana mai cewa yanzu haka samamen haɗin gwiwa na jami’an na gudana “don gano waɗanda suka aikata kisan”.