fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe mataimakin shugaban jami’ar Usman Dan Fodiyo

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun kashe farfesa Yusuf Saidu, mataimakin shugaban sashen bincike da ƙirƙire-ƙirƙire da ci gaba na jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sokoto.

Jami’ar ta sanar da rasuwarsa ne a wata sanarwa da ta fitar a ranar Litinin, inda ta bayyana cewa wasu ‘yan bindiga ne suka kai masa hari tare da kashe shi a lokacin da yake kan hanyarsa daga Sokoto zuwa Kaduna.

“’Yan bindiga sun kai wa farfesa Yusuf Saidu hari tare da kashe shi a kan hanyarsa ta zuwa Kaduna daga jihar Sakkwato.” in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa “Yusuf Saidu mutum ne mai gaskiya da addini da sadaukarwa da kuma jaruntaka.”

Jami’ar ta bayyana rasuwar tasa a matsayin wani rashi mai radadi ga jami’ar da kuma daukacin al’ummar jami’ar, inda suka yi addu’ar Allah ya jikansa da rahama.

Sokoto dai na ɗaya daga cikin jihohin arewa maso yamma da ke fama da matsalar rashin tsaro da ƴan bindiga.

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp