fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe Magidanci a Abuja

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kai hari a unguwar Ushafa da ke karamar hukumar Bwari a Abuja, inda suka kashe wani mutum tare da yin garkuwa da ‘yan uwansa.

Lmarin wanda ya afku a safiyar ranar Laraba da misalin karfe daya na safe ya tayar da hankula a yankin.

Wani dan unguwar, Mista James Olachi, ya shaidawa DAILY POST cewa, lamarin ya faru ne a bayan makarantar firamare ta LGEA Ushafa, kusa da sanannen wurin shakatawa na Going-park.

A cewar Mista James, maharan sun mamaye yankin kuma sun shafe sama da mintuna 30 suna harbe-harbe ba tare da katsewa daga wata hukumar tsaro ba.

Marigayin mai suna Mista Adegoke, an ce ya sha fama da masu garkuwa da mutane kafin a harbe shi.

Maharan da suka kai harin sun tafi da matar da wani dan uwansu zuwa inda ba a san inda suke ba.

Kakakin rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, DSP Josephine Adeh, ba ta amsa kiran wayarta ba, ko kuma ta amsa sakon tes da wakilin DAILY POST ya aike mata.

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...

Na ki marawa Atiku baya ne saboda juyin yankin Kudu ne – Wike

Ministan babban birnin tarayya (FCT), Nyesom Wike, a wata...

An saki sakamakon jarabawar WASSCE

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma ta fitar da...

Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa wajen karbar abinci

Rahotanni daga Gaza na cewa sojojin Isra'ila sun sake...

Ambaliya ya shanye jihohin Bauchi da Filato da kuma Neja

Ambaliya ta cinye gonaki da gidaje da makarantu da...

Najeriya ta lashe gasar kwallon kwandon Afrika

Tawagar ƴan wasan kwando na matan Najeriya ta lashe...

Obi ba zai iya lashe zabe a yankin Arewa ba – Keyamo

Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya ce ɗaya...

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...
X whatsapp