fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe Magidanci a Abuja

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kai hari a unguwar Ushafa da ke karamar hukumar Bwari a Abuja, inda suka kashe wani mutum tare da yin garkuwa da ‘yan uwansa.

Lmarin wanda ya afku a safiyar ranar Laraba da misalin karfe daya na safe ya tayar da hankula a yankin.

Wani dan unguwar, Mista James Olachi, ya shaidawa DAILY POST cewa, lamarin ya faru ne a bayan makarantar firamare ta LGEA Ushafa, kusa da sanannen wurin shakatawa na Going-park.

A cewar Mista James, maharan sun mamaye yankin kuma sun shafe sama da mintuna 30 suna harbe-harbe ba tare da katsewa daga wata hukumar tsaro ba.

Marigayin mai suna Mista Adegoke, an ce ya sha fama da masu garkuwa da mutane kafin a harbe shi.

Maharan da suka kai harin sun tafi da matar da wani dan uwansu zuwa inda ba a san inda suke ba.

Kakakin rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja, DSP Josephine Adeh, ba ta amsa kiran wayarta ba, ko kuma ta amsa sakon tes da wakilin DAILY POST ya aike mata.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp