fidelitybank

‘Yan Bindiga sun kashe jami’in tsaro na sintiri 4 a jihar Anambra

Date:

‘Yanbindiga sun kashe ‘yan ƙungiyar sintiri ta tsaro na jihar Anambra huɗu a yau Litinin.

Uku daga cikin ‘yansintirin an kashe su ne a garin Ukpo da ke ƙaramar hukumar Dunukofia, yayin da ɗayan aka kashe shi a Abatete, da ke ƙaramar hukumar Idemili ta Arewa.

Jarida Daily Trust ta ruwaito cewa ‘yanbindigar sun yi dirar-mikiya ne a garin na Abatete, inda suka buɗe wuta suna harbin kan-mai-uwa-da-wabi, inda suka kashe mutum ɗaya.

Sun kai harin ne bayan da gwamnan jihar Charles Soludo ya bayar da umarni ga ‘yankasuwa su yi watsi da umarnin ‘yan haramtacciyar kungiyar a-ware ta Biafra na zaman gida a duk ranar Litinin, su ci gaba da harkokinsu.

Wani da ya ga yadda aka kai harin ya ce, bayan da ‘yanbindigar suka kashe ‘yan sintirin uku a Ukpo sai suka cinna wa motarsu wuta suka kuma kama mutum wajen bakwai suka tsere da su, tare da raunata wasu da dama.

Kakakin rundunar ‘yansandan jihar ta Anambra SP Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da aukuwar lamarin kuma ya ce babban jami’in ‘yansanda na Ukpo na gudanar da bincike a kai.

A mako biyu da ya gabata Gwamna Soludo ya bayar da umarnin a riƙa buɗe dukkanin kasuwanni a jihar a ranar Litinin, wato a yi watsi da hanin da ƙungiyar ta IPOB ta yi.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp