‘Yanbindiga sun kashe ‘yan ƙungiyar sintiri ta tsaro na jihar Anambra huɗu a yau Litinin.
Uku daga cikin ‘yansintirin an kashe su ne a garin Ukpo da ke ƙaramar hukumar Dunukofia, yayin da ɗayan aka kashe shi a Abatete, da ke ƙaramar hukumar Idemili ta Arewa.
Jarida Daily Trust ta ruwaito cewa ‘yanbindigar sun yi dirar-mikiya ne a garin na Abatete, inda suka buɗe wuta suna harbin kan-mai-uwa-da-wabi, inda suka kashe mutum ɗaya.
Sun kai harin ne bayan da gwamnan jihar Charles Soludo ya bayar da umarni ga ‘yankasuwa su yi watsi da umarnin ‘yan haramtacciyar kungiyar a-ware ta Biafra na zaman gida a duk ranar Litinin, su ci gaba da harkokinsu.
Wani da ya ga yadda aka kai harin ya ce, bayan da ‘yanbindigar suka kashe ‘yan sintirin uku a Ukpo sai suka cinna wa motarsu wuta suka kuma kama mutum wajen bakwai suka tsere da su, tare da raunata wasu da dama.
Kakakin rundunar ‘yansandan jihar ta Anambra SP Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da aukuwar lamarin kuma ya ce babban jami’in ‘yansanda na Ukpo na gudanar da bincike a kai.
A mako biyu da ya gabata Gwamna Soludo ya bayar da umarnin a riƙa buɗe dukkanin kasuwanni a jihar a ranar Litinin, wato a yi watsi da hanin da ƙungiyar ta IPOB ta yi.