Ƴan bindiga sun kashe aƙalla mutum 25 da suka haɗa da Hakimi da wasu sarakunan gargajiya a ƙaramar hukumar Bukkuyyum a jihar Zamfara.
Ƴan bindigar sun afka ƙauyen Ganar Kiyawa ne a ranar Lahadi suka kashe mutanen, kamar yadda mazauna yankin suka shaida wa BBC.
Mutanen garin sun ce, ƴan bindigar sun shiga garin na Ganar Kiyawa ne saman babura, kuma bayan mutane sun tsorata sun fara tserewa, ƴan bindiga suka dinga harbinsu, cikin waɗanda aka kashe har da hakimin garin Bala Muhammadu da Magajin gari Sani Salihu da wani bafade da ake kira Sharu.
“Da ni da Hakimi da Magajin Gari mun yi gudun kilomita uku, kuma da suka cimma Magajin Gari suka tambaye shi me yake wa gudu ya ce wahala, sai suka ce to ta ƙare, suka harbe shi,” a cewar wani mazauni garin da yake bayar da labarin da ƴar magajin garin da aka kashe ta faɗa masu bayan sun tsira.