fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe Dagaci da mutane 6 a Katsina

Date:

Rahotanni daga Jihar Katsina sun tabbatar da cewa, wasu ’yan bindiga sun kai farmaki kauyen Daddara da ke Karamar hukumar Jibiya, inda suka kashe mutum shida, cikinsu har da Dagacin garin.

Maharan sun kuma sace karin wasu mutum biyar, kamar yadda wani daga cikin mazauna kauyen na Daddara ya tabbatar wa Aminiya cewa lamarin ya faru ne a sanyin safiyar ranar Alhamis.

Mutumin, wanda ’yarsa na cikin wadanda maharan suka yi garkuwa da su, ya ce, ’yan bindigar sun kashe Dagacin garin, Alhaji Jafaru Rabi’u, wanda aka fi sani da Magaji Yangayya da kuma yaron gidansa, Malam Nasir Danye.

“Sun kashe Dagaci da hadiminsa da kuma wasu mutane, sannan sun sace ’ya ta da ke aure a garin. A nan babban garin Daddara kuma sun kashe mutum hudu, sannan suka sace wasu, kuma wasu sun jikkata yayin tsira da ransu,’yan bindigar sun shiga cikin gida-gida inda suka saci dabobbi, kayan abinci da kuma kudade daga hannun mutanen da suka shiga gidajensu”. A cewar mutumin.

Ya zuwa lokacin hada wannan rahoton babu wata sanarwa daga rundunar ’yan sandan Jihar ta Katsina, sakamakon, SP Gambo Isah bai daga waya ko amsa rubutaccen sakon kar-ta-kwanan da Aminiya.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp