fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe Dagaci da mutane 6 a Katsina

Date:

Rahotanni daga Jihar Katsina sun tabbatar da cewa, wasu ’yan bindiga sun kai farmaki kauyen Daddara da ke Karamar hukumar Jibiya, inda suka kashe mutum shida, cikinsu har da Dagacin garin.

Maharan sun kuma sace karin wasu mutum biyar, kamar yadda wani daga cikin mazauna kauyen na Daddara ya tabbatar wa Aminiya cewa lamarin ya faru ne a sanyin safiyar ranar Alhamis.

Mutumin, wanda ’yarsa na cikin wadanda maharan suka yi garkuwa da su, ya ce, ’yan bindigar sun kashe Dagacin garin, Alhaji Jafaru Rabi’u, wanda aka fi sani da Magaji Yangayya da kuma yaron gidansa, Malam Nasir Danye.

“Sun kashe Dagaci da hadiminsa da kuma wasu mutane, sannan sun sace ’ya ta da ke aure a garin. A nan babban garin Daddara kuma sun kashe mutum hudu, sannan suka sace wasu, kuma wasu sun jikkata yayin tsira da ransu,’yan bindigar sun shiga cikin gida-gida inda suka saci dabobbi, kayan abinci da kuma kudade daga hannun mutanen da suka shiga gidajensu”. A cewar mutumin.

Ya zuwa lokacin hada wannan rahoton babu wata sanarwa daga rundunar ’yan sandan Jihar ta Katsina, sakamakon, SP Gambo Isah bai daga waya ko amsa rubutaccen sakon kar-ta-kwanan da Aminiya.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

APC ta yi kwaf daya a zaben cike gurbin Kaduna da Jigawa

Jam'iyyar APC mai mulki a jihar Jigawa ta yi...

Ba mu yarda da zaben Ghari da Tsanyawa ba – NNPP

Jam'iyar NNPP mai mulkin jihar Kano a arewacin Najeriya...

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...
X whatsapp