fidelitybank

‘Yan bindiga sun kashe babban Limamin juma’a a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun sake kai hari jihar Zamfara, inda suka kashe Sheikh Ahmad Rufa’i, babban limamin babban masallacin Juma’a na kauyen Keita a karamar hukumar Tsafe a jihar.

Harin ya faru ne jim kadan bayan musulmi sun yi sallar isha’i (dare) a jam’i.

Wannan mummunan lamari dai ya zo ne makonni uku kacal bayan kisan da aka yi wa Imam Abubakar Hassan Mada babban limamin babban masallacin garin Mada, karamar hukumar Gusau.

A cewar Ibrahim Musa Keita, wani mazaunin kauyen Keita, an fara ganin barayin ne a kan hanyar Kwarin Gano zuwa Keita.

Duk da an sanar da mazauna garin, ‘yan fashin sun ci gaba da mamaye kauyen.

Bayan sun kasa sace masu amfani da hanyar, sun kai hari kauyen Keita, inda suka kashe babban limamin, tare da yin awon gaba da mutane da dama ciki har da mata.

“Kafin mamayar, an sanar da mazauna garin game da motsin ‘yan bindigar a kan titin Kwarin Gano-Keita.

“An hango su a kan hanyar amma ba mu da tabbacin ko za su zo wannan kauyen ko a’a.

“Da farko sun so su yi awon gaba da masu amfani da hanyar a kan hanyar Keita zuwa Kwarin Gano, amma bayan sun dauki lokaci ba tare da samun ko mutum daya ba, sai suka mamaye kauyen Keita, suka kashe babban limamin mu tare da sace mutane da dama ciki har da mata.

“Ba mu tantance adadin mutanen da suka yi garkuwa da su ba yayin da wasu suka ruga cikin daji har yanzu ba a gansu ba.” Ya bayyana.

A wani labarin kuma, an yi garkuwa da wasu mutane biyu a kauyen Magazu dake karamar hukumar Tsafe da sanyin safiyar Talata.

‘Yan bindigar a cewar wani mazaunin kauyen Yusuf Ibrahim, sun mamaye kauyen ne da misalin karfe uku na safe, inda suka rika harbe-harbe.

Ibrahim ya kara da cewa yawancin mazauna garin sun bar gidajensu.

Wani mazaunin kauyen Kwalfada, Aminu Kwalfada, ya koka kan yadda fargabar ‘yan bindiga ke sa jama’a daina amfani da lasifika a masallatai a lokutan sallah.

ASP. Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, Abubakar Yazid, bai iya bayar da cikakken bayani ba har zuwa lokacin da aka bayar da rahoton, amma ya yi alkawarin bayar da bayanai da zarar an samu.

latest nigeria newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp