Wasu ‘yan bindiga sun sake kai hari jihar Zamfara, inda suka kashe Sheikh Ahmad Rufa’i, babban limamin babban masallacin Juma’a na kauyen Keita a karamar hukumar Tsafe a jihar.
Harin ya faru ne jim kadan bayan musulmi sun yi sallar isha’i (dare) a jam’i.
Wannan mummunan lamari dai ya zo ne makonni uku kacal bayan kisan da aka yi wa Imam Abubakar Hassan Mada babban limamin babban masallacin garin Mada, karamar hukumar Gusau.
A cewar Ibrahim Musa Keita, wani mazaunin kauyen Keita, an fara ganin barayin ne a kan hanyar Kwarin Gano zuwa Keita.
Duk da an sanar da mazauna garin, ‘yan fashin sun ci gaba da mamaye kauyen.
Bayan sun kasa sace masu amfani da hanyar, sun kai hari kauyen Keita, inda suka kashe babban limamin, tare da yin awon gaba da mutane da dama ciki har da mata.
“Kafin mamayar, an sanar da mazauna garin game da motsin ‘yan bindigar a kan titin Kwarin Gano-Keita.
“An hango su a kan hanyar amma ba mu da tabbacin ko za su zo wannan kauyen ko a’a.
“Da farko sun so su yi awon gaba da masu amfani da hanyar a kan hanyar Keita zuwa Kwarin Gano, amma bayan sun dauki lokaci ba tare da samun ko mutum daya ba, sai suka mamaye kauyen Keita, suka kashe babban limamin mu tare da sace mutane da dama ciki har da mata.
“Ba mu tantance adadin mutanen da suka yi garkuwa da su ba yayin da wasu suka ruga cikin daji har yanzu ba a gansu ba.” Ya bayyana.
A wani labarin kuma, an yi garkuwa da wasu mutane biyu a kauyen Magazu dake karamar hukumar Tsafe da sanyin safiyar Talata.
‘Yan bindigar a cewar wani mazaunin kauyen Yusuf Ibrahim, sun mamaye kauyen ne da misalin karfe uku na safe, inda suka rika harbe-harbe.
Ibrahim ya kara da cewa yawancin mazauna garin sun bar gidajensu.
Wani mazaunin kauyen Kwalfada, Aminu Kwalfada, ya koka kan yadda fargabar ‘yan bindiga ke sa jama’a daina amfani da lasifika a masallatai a lokutan sallah.
ASP. Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, Abubakar Yazid, bai iya bayar da cikakken bayani ba har zuwa lokacin da aka bayar da rahoton, amma ya yi alkawarin bayar da bayanai da zarar an samu.