fidelitybank

‘Yan Bindiga sun kai hari mahaifar gwamnan Taraba

Date:

Rundunar yan sandan jihar Taraba ta tabbatar da harin da yan bindiga suka kai wa mahaifiyar gwamnan jihar da kanwarsa.

An samu rahoton kai hari kan mahaifiyar Agbu Kefas,, Jummai Kefas da kanwarsa mai suna Atsi Kefas a titin Kente a karamar hukumar Wukari.

Kakakin rundunar, Usman Abdullahi ya tabbatar da afkuwar lamarin a ranar Juma’a, kamar yadda reshen rundunar a Wukari ya tabbatar masu.

Ya bayyana cewa sun samu rahoton yan fashi da makami sun kai hari kan matafiya a hanyar, amma ba a sanar da su cewar dangin gwamnan jihar ba ne.

“Ana binciken lamarin, kuma ana sa ran hukunta wadanda su ka tafka wannan danyen aiki,” inji shi.

Kawo yanzu, gwamnan jihar bai ce komai a kan lamarin ba a hukumance, amma sakataren gwamnati, Timothy Kataps ya ta bayyana labarin a matsayin labarin karya.

Amma wasu daga cikin iyalan gwamnan da su ka nemi a boye sunansu, sun tabbatar da harin, kuma an bayyana cewa ana duba lafiyar mahaifiyar gwamnan.

bbc nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp