A ranar Laraba ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari kauyen Boto da ke karamar hukumar Tafawa Balewa a jihar Bauchi, inda suka kashe mutum daya tare da yin garkuwa da wasu uku.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da ‘yan sandan jihar, Ahmed Wakili, ya fitar ranar Alhamis a Bauchi.
“Mun samu labarin cewa ‘yan bindiga da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne sun kai farmaki kauyen Boto.
“Nan take kwamishinan ‘yan sandan, Umar Sanda ya umurci jami’in ‘yan sanda reshen Tafawa Balewa da ya zage damtse.
“DPO ya tattara mutanensa suka garzaya kauyen amma ‘yan bindigar sun tafi tare da wadanda aka kashe.
“Yanzu haka mutanenmu suna ta tseguntawa lungu da sako domin neman masu laifin. In sha Allahu za mu kama su mu gurfanar da su a gaban kuliya,” inji shi.