Kasa da kwanaki hudu a gudanar da babban zaben watan Fabrairu, wasu ‘yan bindiga da ba a tantance ba, sun kai hari tare da tarwatsa ofisoshin gudanarwa na karamar hukumar Okehi ta jihar Kogi.
DAILY POST ta tattaro cewa lamarin ya faru ne a daren ranar Litinin lokacin da maharan suka mamaye yankin da wasu bama-bamai.
Karanta Wannan: ‘Yan Sanda na neman mamban NYSC ruwa a jallo
Da aka tuntubi DAILY POST, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kogi, William Ovye Aya, ya tabbatar da faruwar lamarin.
A cewarsa, rundunar ta fara gudanar da bincike domin gano musabbabin harin.
Idan za a iya tunawa, kungiyar Boko Haram da ke samun goyon bayan kungiyar IS, ISWAP, ta dauki alhakin harin bam da aka kai cikin wata mota da ya yi sanadin mutuwar mutane kusan hudu tare da jikkata wasu da dama a karamar hukumar Okene ta jihar Kogi a watan Janairu.