fidelitybank

‘Yan bindiga sun kai hari kan Okowa tare d kashe jami’an tsaro 3

Date:

‘Yan bindiga sun yi wa tawagar jami’an tsaron ɗan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar PDP Ifeanyi Okowa kwanton ɓauna tare da kashe ‘yan sanda uku.

Rahotonni sun ce maharan sun far wa tawagar jami’an tsaron lafiar gwamnan, da suka hada da ‘yan sanda huɗu a daidai garin Ihiala da ke ƙaramar hukumar Ihiala ta jihar Anambra.

Wasu majiyoyi sun ce jami’an tsaron na kan hanyarsu ta zuwa jihar Abia, inda tsara mista Okowa zai je domin ganawa da wasu mambobin jam’iyyar PDP a jihar gabanin babban zaɓen ƙasa da ke tafe ranar 25 ga watan da muke ciki.

Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta tabbatar da faruwar lamarin.

A jerin wasu saƙonni da ya wallafa a shafinsa na Tuwita ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasar Ifeanyi Okowa ya miƙa sakon ta’aziyyar gwamnatin jihar da iyalansa zuwa ga iyalan mamatan, waɗanda ya bayyana a matsayin ‘jajirtattu’.

Tare da yin addu’ar samun rahama a gare su, sannan kuma yi alƙawarin nema wa iylansu haƙƙinsu.

Harin dai na zuwa ne kwana guda bayan da wasu ‘yan bindiga suka kai hari kan tawagar daraktan yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP na jihar Rivers a birnin fatakwal.

latest news in nigeria today 
2021 ripples

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp