fidelitybank

‘Yan bindiga sun kai hari kan Okowa tare d kashe jami’an tsaro 3

Date:

‘Yan bindiga sun yi wa tawagar jami’an tsaron ɗan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar PDP Ifeanyi Okowa kwanton ɓauna tare da kashe ‘yan sanda uku.

Rahotonni sun ce maharan sun far wa tawagar jami’an tsaron lafiar gwamnan, da suka hada da ‘yan sanda huɗu a daidai garin Ihiala da ke ƙaramar hukumar Ihiala ta jihar Anambra.

Wasu majiyoyi sun ce jami’an tsaron na kan hanyarsu ta zuwa jihar Abia, inda tsara mista Okowa zai je domin ganawa da wasu mambobin jam’iyyar PDP a jihar gabanin babban zaɓen ƙasa da ke tafe ranar 25 ga watan da muke ciki.

Rundunar ‘yan sandan jihar Anambra ta tabbatar da faruwar lamarin.

A jerin wasu saƙonni da ya wallafa a shafinsa na Tuwita ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasar Ifeanyi Okowa ya miƙa sakon ta’aziyyar gwamnatin jihar da iyalansa zuwa ga iyalan mamatan, waɗanda ya bayyana a matsayin ‘jajirtattu’.

Tare da yin addu’ar samun rahama a gare su, sannan kuma yi alƙawarin nema wa iylansu haƙƙinsu.

Harin dai na zuwa ne kwana guda bayan da wasu ‘yan bindiga suka kai hari kan tawagar daraktan yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP na jihar Rivers a birnin fatakwal.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp