Wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari kan wasu magoya bayan ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregebsola, a karkashin jam’iyyar APC.
Rahotanni sun nuna cewa an kai wa magoya bayan Aregbesola hari ne a ranar Talata a wani taron siyasa a Ikirun.
‘Yan kungiyar Progressive Osun, a karkashin jam’iyyar APC ta Osun, sun ce suna gudanar da taro ne a gefen sakatariyar karamar hukumar Ifelodun a lokacin da ‘yan bangar suka far musu.
Da yake mayar da martani game da lamarin, sakataren jam’iyyar TOP na jihar, Adelani Baderinwa, ya ce, ‘yan bindigar kusan mutane 25 ne suka ta harbin iska tare da yin barazanar yin amfani da adduna ga ‘ya’yan jam’iyyar.
Ya ce, “Muna gudanar da taron mu na mazabar tarayya ta Ifelodun/Boripe/Odo-Otin, wadanda adadinsu ya kai kusan 25, sun fito ne daga cikin Sakatariyar Karamar Hukumar, suka fara korar mutanen mu”.