‘Yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun sace masu bauta tara a wani coci a ƙaramar hukumar Kankara a jihar Katsina.
Rahotonni sun ce ‘yan bindigar sun je cocin ne da ke unguwar Gidan Haruna a kan babura da safiyar ranar Lahadi a lokacin da masu bautar ke gudanar da addu’o’insu.
Reveran Yusuf Haruna shugaban ƙungiyar CAN reshen ƙaramar hukumar Kankara ya shaida wa BBC cewa ‘yan bindigar sun sace mutum tara ciki har da mata bakwai da yara biyu.
Ya ƙara da cewa maharan sun daki wani magidanci tare da karya shi a lokacin da suka kai harin.
Jihar Katsina dai na daga cikin jihohin arewacin ƙasar da ‘yan bindiga ke cin karensu babu babbaka.
A watan Disamban 2020 ‘yan bindiga sun kai wani hari makarantar sakandiren Kankara tare da yin garkuwa da ɗalibai 300, waɗanda daga baya a ka sako su.