fidelitybank

‘Yan bindiga sun harbe tsohon jami’in gwamnatin Jigawa

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne a ranar Talata da daddare sun harbe wani tsohon babban manajan hukumar gidaje ta jihar Jigawa, Babangida Abubakar Sadeeq da wasu mutane biyu.

Wani mazaunin garin ya shaidawa manema labarai cewa, lamarin ya faru ne a kan hanyar Yalwandamai, yayin da tsohon jami’in gwamnatin ke kan hanyar Birnin Kudu, garinsu bayan ya bar gonarsa da ke Dutse.

A cewar majiyar: “Marigayi Babangida yana dawowa daga Dutse, sai ya yi reshe zuwa wani kauye kusa da Yalwandamai domin ganin mutanensa da ke aiki a gonarsa.

“Ba da dadewa ya bar gonar ba, wasu ’yan mitoci, daya daga cikin mutanen da ke cikin motarsa ya lura suna zuwa wajen wasu mutane, sai ya yi gaggawar sanar da Babangida.

“Babangida, wanda ke tuka motar ya canza zuwa ga cikakken haske don ganin baƙon; da suka ga cikakken hasken, sai suka bude wuta kan motar da ke tafiya.”

Ya ce an kai Babangida da sauran su zuwa cibiyar kula da lafiya ta tarayya dake Birnin Kudu, kuma likita ya tabbatar da mutuwar su.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, DSP Lawan Shiisu, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce ana ci gaba da kokarin cafke wadanda suka aikata laifin.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp