Rahotanni sun ce wasu ‘yan bindiga sun kashe mutum daya a wani hari da suka kai a karamar hukumar Sabon Gari da ke jihar Kaduna.
Wanda aka kashe din mai suna Yarima Mohammed na kauyen Kufena Wusasa, an kashe shi ne a lokacin da ya bijirewa ‘yan bindigar a yayin da ake yin garkuwa da su.
Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna da ta tabbatar da faruwar harin ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta fitar.
A cewar kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Mohammed Jalige, ‘yan bindigan sanye da kakin sojoji, dauke da manyan muggan makamai sun mamaye yankin Gabari da ke yankin Samaru a Sabon Gari, inda suka fara harbe-harbe ba da dadewa ba, inda suka yi ta harbin mutane hudu cikin dajin.
Da samun bayanan, nan take suka tura mutanen Operation Puff Adder II da ’yan banga na gida; wadanda cikin karfin hali suka yi kwanton bauna kan hanyar da ‘yan bindigar za su bi tare da samun nasarar kubutar da wasu mutane biyu da ‘yan fashin suka yi garkuwa da su.