fidelitybank

‘Yan bindiga sun harbe liamamin masallaci a Kaduna

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun harbe babbar matar babban limamin masallacin makiyaya da ke Rugan Ardo, Isyaka Adamu, har lahira.

Misis Hulaira Hussaini Ardo, an harbe ta ne bayan ‘yan fashin sun karbi Naira miliyan 2 a matsayin kudin fansa.

Tun a ranar 11 ga Fabrairu, 2023, ‘yan bindiga sun sace matan Malam Husaaini Ardo hudu a Rugan Ardo a karamar hukumar Kagarko, suka kashe babban limamin masallacin makiyaya da ke Rugan Ardo, Isyaka Adamu.

Madaki na Janjala, Samaila Babangida, ya tabbatar da kisan, kuma ya ce al’ummar garin na cikin alhinin kashe matar sarkinsu, inda ya ce barayin sun ki sakin gawar ta.

A cewarsa, an biya kudin fansa naira miliyan 2 domin sakin matan hudu, amma ‘yan fashin sun harbe babbar matar, yayin da sauran ukun suka sako.

Ya ce bayan an kai kudin fansa ga ‘yan fashin tare da ba da tabbacin ‘yantar da matan sarki hudu ne shugaban ‘yan bindigar ya harbe babbar matar tare da sakin sauran ukun.

“Na hau daya daga cikin baburan da ya kai musu kudi da kayan abinci. Bayan sun karbi kudin ne shugabansu ya bude wa babbar matar wuta,” inji shi.

Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan, DSP Mohammed Jalige bai amsa kiran da aka yi masa ba da kuma sakon da aka aike masa

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp