fidelitybank

‘Yan bindiga sun harbe hadimin mataimakin shugaban majalisar dattawa

Date:

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Ovie Omo-Agege ,ya rasa daya daga cikin hadiman sa.

Wasu ‘yan bindiga sun harbe Cyril Mudiagbe a garin Sapele da ke karamar hukumar Sapele a jihar Delta.

Wanda aka fi sani da Cyril Makanaki, dan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ne da ke Ward 6 a Sapele.

Lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Lahadi a gidansa da ke unguwar Decima.

Wani makwabci mai suna Eniagbe ya ce ‘yan bindigar sun harbe marigayin ta tagar.

“Suna buga tagar sa kuma lokacin da ya bude tagar, an harbe shi a kirji”, in ji shi.

Jami’an tsaro da suka hada da ‘yan banga sun fara farautar maharan.

Jami’in hulda da jama’a na ‘yan sanda,a Delta, Bright Edafe ya ce har yanzu bai samu cikakken bayani kan lamarin ba.

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp