fidelitybank

‘Yan bindiga sun harbe Basarake a Taraba

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba, a daren ranar Alhamis, sun kashe wani basarake mai daraja ta uku, Abdulmutalib Nuhu, a kauyen Sensani da ke karamar hukumar Gasol a jihar Taraba.

An tattaro cewa an kashe Nuhu ne sa’o’i kadan kafin gudanar da bikin kamun kifi da al’adu na Nwonyo da gwamnatin jihar Taraba ta shirya a karamar hukumar Ibbi ta jihar.

DAILY POST ta tattaro cewa Ibbi mahaifar Hamisu Bala ne, wanda aka fi sani da Wadume, fitaccen dan tseren bindiga, wanda aka sako daga gidan yari kwanakin baya.

Maharan sun kai farmaki kauyen Sensani ne da misalin karfe 9 na daren ranar Alhamis, inda suka nufi fadar sarkin gargajiya, mai tazarar kilomita kadan daga Ibbi, wurin da aka gudanar da bikin.

Sai dai gwamnatin jihar Taraba ta baiwa mutanen da ke balaguro tabbacin samun isasshen tsaro a yayin bikin.

Kanin sarkin da aka kashe, Nuhu Sanseni, ya shaidawa manema labarai cewa ‘yan bindigar sun zo ne a kan babura dauke da bindigogi, inda suka kashe dan uwansa, sannan suka tafi da wayoyinsa.

“Sun zo unguwar ne da misalin karfe 9 na daren jiya, kai tsaye suka je fadar sa, suka harbe shi, suka kwace masa wayoyinsa guda biyu. Suna cikin tafiya sai suka gamu da wani matashi da ke zuwa a kan babur, shi ma sun harbe shi suka karya masa kafa kafin su bar kauyen.” Inji Sansani.

Wani babban jami’in ‘yan sanda da ke aiki a Sansani ya bayyana wa wakilinmu cewa tuni mutanen nasa suna bin wadanda suka kashe.

Mukaddashin jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Taraba, ASP James Lashen, da aka tuntube shi, ya ce har yanzu yana kan hanyarsa ta zuwa ofishin har zuwa lokacin da aka samu rahoton a ranar Juma’a.

“Ban sani ba. Ina kan hanyara ta zuwa ofis yanzu, idan na sami rahoton halin da ake ciki, zan sanar da ku, ”in ji Lashen.

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp