Yan bindiga sun kashe wani Ladani yayin da yake tsaka da cikin kiran sallar Asuba a ƙauyen Magazu, dake karamar hukumar Tsafe, a jihar Zamfara.
Mazauna ƙauyen sun shaida wa jaridar Daily Trust cewa, Ladanin ya na cikin Masallaci ya na kiran Sallah, lokacin da ‘yan bindigan suka shigo kuma suka harbe shi har ya rasu.
Ƙauyen Magazu, na da nisan kilomita 40 daga ɓangaren kudancin Gusau, babban birnin jihar Zamfara, kuma ya na kan hanyar Gusau zuwa Funtua ta jihar Katsina.
Tun bayan tsintar gawar wani ɗan bindiga a bayan gari kwanan nan, ‘yan ta’addan suka jefa kauyen cikin halin rashin tabbas da zaman ɗar-ɗar.
Bayan haka ne, ‘yan ta’adda suka sha alwashin ɗaukar fansar ɗan uwansu da aka kashe, wanda suka ɗora laifin kan mazauna ƙauyen Magazu.