Rahotanni sun bayyana cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kashe wani dan sanda a titin Edgerton, Calabar, jihar Cross River.
Rundunar ‘yan sandan Kuros Riba wadda ta tabbatar da faruwar lamarin ta bayyana jami’in da ya rasu a matsayin Sgt. Peter Ikwen,
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Irene Ugbo, ya ce maharan sun dauki bindigar dan sandan.
“Dazun nan na tattaro cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun harbe wani Sajan dan sanda da sanyin safiyar yau (Asabar) kuma maharan sun dauke bindigarsa,” inji ta.
Ta shaida wa NAN cewa an fara gudanar da bincike da nufin bankado wadanda suka aikata wannan aika-aika wanda ta bayyana a matsayin abin Allah wadai.