Ƴan bindiga sun tare hanyar Koko zuwa Yauri, a jihar Kebbi a ranar Asabar.
Dan majalisar tarayya da ke wakiltar yankin, Hon Tanko Yusuf Sununu ya tabbatar wa BBC cewa, lokacin ya na tsaye kan hanyar da aka rufe, sun shiga cikin tashin hankali.
Ya ce, sun shafe awanni ƴan bindigar na cin karensu ba babbaka a kan babbar hanyar da ta haɗa Kebbi da jihar Neja.
Ƴan bindigar sun tarwatsa mutanen garuruwan Kimo da Laka da Birnin Yauri yawancinsu mata da ƙananan yara kafin suka tare hanyar shiga garin Bakin Turu kuma suka yi wa garin ƙawanya, a cewar ɗan majalisar.
A Yankin Yauri, ƴan bindiga suka shiga suka saci ɗalibai kuma yanzu matsalar tsaro a yankin na ƙara ƙamari.
Wasu rahotanni kuma sun ce, ƴan bindiga sun mamaye wasu ƙauyuka na Rijau a jihar Neja.