fidelitybank

‘Yan bindiga sun bukaci a basu Naira miliyan 500 su saki mutane 30 a Zamfara

Date:

‘Yan bindigan da suka yi garkuwa da mutane sama da 30 a baya-bayan nan a karamar hukumar Maradun, jihar Zamfara, mahaifar karamin ministan tsaro, Hon. Bello Mohammed Matawalle, ya bukaci a biya Naira miliyan 500 a matsayin kudin fansa.

Wani mazaunin yankin mai suna Ibrahim Maradun ya shaidawa manema labarai, cewa duk wata hanya da ake da ita don tara kudin ta zama tabarbare saboda masu hannu da shuni ba su nuna damuwar biyan kudin fansa ba.

“Muna da attajirai a garin amma ba za su iya yin kasada da dukiyoyinsu ba domin wadanda aka sace su kwato ‘yancinsu daga ‘yan bindigar,” in ji shi.

Maradun ya bayyana cewa tun da lamarin ya faru, gwamnatin jihar da hukumomin tsaro ba su bayar da wata sanarwa a hukumance ba.

“Gwamnatin jihar ba ta ziyarci garin don nuna juyayi ba, haka kuma Gwamnan bai wakilta wani jami’in gwamnati don nuna damuwa ba,” in ji shi.

Maradun ya lura cewa al’ummar yankin sun yi wa tsohon Gwamna Matawalle tawaye ta hanyar akwatin zabe saboda rashin tsaro.

“A yayin yakin neman zabe, Gwamna Dauda Lawal ya tabbatar wa da masu zabe cewa idan aka zabe shi a kan mulki, zai kawo karshen ayyukan ‘yan fashi a cikin kwanaki 100 na mulki.

“Amma yanzu, lamarin yana kara ta’azzara yayin da ayyukan ‘yan bindiga ke ci gaba da ta’azzara ba tare da la’akari da hakan ba.

“Kwanan nan, ‘yan bindiga sun yi wa jami’an tsaron jihar kwanton bauna, da aka fi sani da Community Protection Guard, CPG, sun kashe uku daga cikinsu, suka raunata da dama tare da kwace musu makamai,” in ji shi.

Ya yi kira ga gwamnatin jihar da jami’an tsaro da su kara zage damtse wajen ganin an sako mutanen da aka sace.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp