Kimanin mutane biyar sun rasa rayukan su a lokacin da ‘yan bindiga suka kai farmaki a wuraren zabe guda biyu yayin gudanar da zaben karamar hukumar jihar Enugu a ranar Laraba.
An gano cewa miyagun sun budewa jama’a wuta a yayin da suka fito zabe a gunduma ta uku da ke karamar hukumar Enugu ta kudu Ganau ya sanar da yadda suka dinga jiyon muryoyin ‘yan bindigan yayin da suke daga muryar cewa sun hana jama’a fitowa zabe.
‘Yan bindigan sun auka wa akwatin zabe a gunduma ta uku a akwatin zaben dake Akpugo cikin Nkanu dake karamar ta karamar hukumar ta Yamma, Daily Trust ce ta rawaito.