fidelitybank

‘Yan bindiga na yin dabaru wajen kai hare0hare a Zamfara – Sojoji

Date:

Rundunar sojojin Najeriya ta fitar da wata sanarwa inda ta ke cewa wasu ‘yan ta’adda da ke kai hare-hare a shiyar Arewa maso yamma da Arewa ta tsakiya na amfani da wasu hanyoyin yaudara da za su iya kai ga tayar da rikici a ƙasa.

Bayanin ya ƙara da cewa akwai hujjojin da ke nuna cewa ‘yan ta’addan na amfani da dabarun dasa nakiya da sauran abubuwa masu fashewa wajen kai hare-hare, abinda zai jefa tsoro cikin zuƙatan mutane.

Sai dai rundunar sojojin ta ce a shirye ta ke domin bankaɗo duk wani makirci da ‘yan ta’addan ke amfani da shi ko da kuwa ya kasance mai tsanani.

Babban hanfsan sojojin Najeriya Laftanar Janar Taoreed Abiodun Lagbaja ne ya sanar da hakan a ranar Jumu’a a helkwatar Sojoji da ke Abuja, lokacin da ya ke karɓar baƙuncin mai taimakawa Babban Sakataren Majalisar Ɗunkin kan sha’anin yaƙi da ayyukan ta’addanci, Vladimir Voronkov.

Babban hafsan sojojin ya kuma ce a shirye rudunar ta ke don yin haɗin gwiwa da Majalisar Ɗunkin Duniyar don ganin an maido da zaman lafiya a yankunan ƙasar.

Ya ce za su yi amfani da kowane mataki da ya dace domin tabbatar da nasarar hakan.

Ya kuma nemi tallafin Majalisar Ɗunkin Duniyar da sauran hukumomi masu zaman kansu domin ɗaukar matakin da ya fi dacewa ga tubabbun ‘yan ta’adda.

Mai taimakawa Babban Sakataren Majalisar Ɗunkin Duniya, Vladimir Voronkov, ya sha alawashin cewa hukumarsa za ta tallafawa Najeriya wajen gano da kuma gurfanar da masu aikata muggan laifuka.

natforce latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp