fidelitybank

‘Yan Bindiga ku mika wuya ko a cigaba da yi muku ruwan wuta – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya ce za, a cigaba da luguden wuta a kan ƴanbindiga da ɓarayin daji da masu satar man fetur da sauran ɓata-garin da suke addabar Najeriya matuƙar ba su daina ta’addancin da suke yi ba.

Tinubu ya bayyana haka ne a jiya Alhamis a cibiyar samun horo na sojoji ta Army Resource Center da ke Abuja a wajen taron tattaunawa a kan matsalolin tsaro a Najeriya da hanyoyin magance su wanda kamfanin dillanci na Najeriya NAN ya shirya a ƙarƙashin jagorancin Janar Abdulsalami.

Tinubu wanda ya samu wakilcin mai ba shi shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya ce, “shekara 15 ke nan muna fama da rashin tsaro a Najeriya. Mugayen mutane suna yadda suke so. Amma yanzu lokaci ya zo da dole su dakata haka.

“A cikin shekara ɗaya, an kashe sama da kwamandojin Boko Haram 300, sannan an samu sauƙin garkuwa da mutane domin kuɗin fansa. Don haka wannan gargaɗi ne gare su, sun dai ga yadda aka yi da kwamandojinu, don haka idan suka ƙi miƙa wuya, za su fuskanci abun da ya faru da jagororinsu.

“Ƙofarmu a buɗe take ga duk wanda yake so ya miƙa wuya, idan ba haka ba kuma, sun san abin da zai biyo baya,” in ji shi.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp