Gwamnatin Jihar Neja ta ce, jami’an tsaro sun kashe ‘yan bindiga 200 cikin kwana huɗu da suka gabata.
Kwamashinan Ƙananan Hukumomi Emmanuel Umar ya bayyana cewa, dakarun tsaron sun fafata ne da yaran riƙaƙƙun ‘yan fashin daji da suka haɗa da Ali Kawajo, da Bello Janbros, da Kachalla Halilu, da kuma Bello Turji.
A cewarsa, an ƙwato babur 60 da kuma shanun da ba a san adadinsu ba daga hannun ‘yan fashin, inda aka mayar wa masu su kayansu.
Ya ƙara da cewa, an yi fafatawar a yankunan Kundu da Babanlaba na ƙananan hukumomin Rafi da Mariga tsakanin Lahadi zuwa Laraba da suka wuce.
Jami’an tsaro biyu ne suka rasa rayukansu yayin gumurzun, in ji kwamashinan.