Wasu ‘yan bindiga sun kai hari kan rukunin gidaje na low-cost da ke Ƙaramar Hukumar Zaria ta Jihar Kaduna tare da yin garkuwa da wani jami’in hukumar Kwastam.
Rahotanni sun ce maharan sun kutsa unguwar da misalin ƙarfe 8:00 na yammacin Laraba, inda suka buɗe wuta kan mai tsautsayi.
Daga baya sun wuce kai-tsaye zuwa gidan ofisan tare da tafiya da shi da kuma ɗansa.
Kafar yaɗa labarai na Channels TV ta ruwaito cewa,n ‘yan bindigar sun sace ƙarin wasu mutum shida.
Lamarin ya faru kwana biyu bayan wasu ‘yan bindiga sun kashe mutum aƙalla takwas da jikkata kusan 30 a harin da suka kai kan jirgin ƙasa na Kaduna zuwa Abuja. Kazalika, sun sace mutanen da har yanzu ba a tantance yawansu ba.