A ranar Asabar ne wasu da ake zargin ‘yan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ne suka kai wa wasu ma’aikatan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC da mamba mai yi wa kasa hidima NYSC hari a yayin zaben gwamna a jihar Bayelsa.
‘Yan barandan sun kuma kwashe kayan zaben da suka hada da BVAS na Ward 1, Unit 23, dake Onopa a karamar hukumar Yenagoa a jihar.
Haka kuma wasu ‘yan baranda sun kwashe jakar da sauran kayan dan sandan.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, wakilin jam’iyyar PDP, ya ce ana ci gaba da tattara kuri’u a lokacin da ‘yan baranda suka mamaye sashin. Ya kuma tabbatar da cewa babu wanda ya jikkata a lamarin.
Hakazalika, a Ward11 na Opume da Emakalakala a karamar hukumar Ogbia a jihar, wasu da ake zargin ‘yan daba ne na jam’iyyar APC sun yi kaca-kaca da rumfunan zabe 14,15 da 19, lamarin da ya kawo cikas ga zaben.
Amma an yi rikodin wasu sakamakon kafin a rushe tsarin.
Hakazalika, a Unguwa ta 3 a unguwar Olodiama da ke karamar hukumar Ijaw ta Kudu a jihar, wasu ‘yan baranda sun yi awon gaba da ainihin sakamakon zaben mazabu 14,15,16,17,18 da 19.