Ma’aikatar harkokin wajen Rasah ta ce, dakarun ‘yan aware na lardin Donesk da ya ayyana ‘yancin kansa sun kama garin Volnovakha da ke tsakanin Donesk din da kuma birnin Mariupol da aka yiwa kawanya.
Wata ‘yar jarida a birnin ta bayyana cewa @an kai hare-hare har ta sama har uku da fashewar abubuwa miniti 13 daga inda nake tsaye kuma jami’an kashe gobara na ta kokari wajen kashe wutar wajen”.
Mutum ɗaya ya mutu nan take, akwai kuma hari ta sama da ya fada a wata makarantar yara.
Mai Magana da yawun rundunar, Igor Konashenkov, ya bayyana a kafar talbijin din kasar cewa dakarun ‘yan awaren sun yi wa Mariupol kofar rago. A cewar BBC.