fidelitybank

‘Yan adawa ba za ku gane karfin APC ba sai ranar zabe – Badaru

Date:

Gwamnan jihar Jigawa, Muhammad Badaru Abubakar, ya ce, jam’iyyun adawa za su fahimci banbancin jam’iyyar da jama’a suka zaba da kuma wadanda ake raina a zaben 2023.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da yake jawabi ga dimbin jama’a a karamar hukumar Kaugama. Ya kuma mayar da martani ne kan lalata fastoci da allunan talla na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da ake zargin jam’iyyun adawa sun yi.

Ya ce jam’iyyar APC mai mulki a jihar ta samar da fili mai kyau ga daukacin jam’iyyun adawa na jihar.

A cewarsa: “Abin takaici ne matuka, a matsayinmu na jam’iyyar da ke mulki, ba mu ci zarafin kowa ba, ba mu lalata fosta da allunan wata jam’iyya ba, har yanzu wasu jam’iyyun adawa suna lalata namu.

“Jam’iyya mai karfi ba za ta shiga cikin wani fada ko lalata dukiyoyin ‘yan adawa ba amma kawai tana nuna bambance-bambance a ranar zabe.”

Badaru, ya kuma kara da cewa jam’iyyun adawa za su fahimci bambancin da ke tsakanin jam’iyyar da ta zabi jama’a da kuma wadanda aka raina.

Barnata allunan tallan na APC, ya bayyana cewa, ba zai shafi farin jinin jam’iyyar ba, illa kara yawan magoya bayanta.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp