fidelitybank

Yakin Ukraine: An kashe dalibin Zambia da ya ke tallafawa Rasha

Date:

Wani ɗalibi ɗan asalin Zambia wanda ke karatu a Rasha, ya rasa ransa a fagen yaƙi a Ukraine, a wani yanayi mai ɗaure kai.

Ministan tsaro na Zambia ya shaida wa manema labaru a Lusaka cewa, dama dai ɗalibin yana zaman kaso ne a ƙasar ta Rasha.

Ɗalibin mai suna Lemekhani, mai shekara 23, yana karantar ilimin nukiliya ne a Moscow Engineering Physics Institute, amma a shekarar 2020 an yanke masa ɗaurin shekara tara bayan samun sa da wani laifi da ba a fayyace ba.

Ministan harkokin wajen na Zambia, Stanley Kakubo, ya faɗa wa manema labarai a yau Litinin cewa, Nyirenda, wanda ɗaya ne daga cikin ɗaliban da gwamnati ke ɗaukar nauyin karatunsu a ƙasar ta Rasha, an kashe shi ne tun cikin watan Satumba, amma sai yanzu ne hukumomin Rasha suka sanar da ƙasar ta Zambia.

Ya ce saboda haka “gwamnatin Zambia ta buƙaci Rasha ta yi mata bayani dalla-dalla kan yadda aka yi ɗalibin da ke zaman kaso ya samu kansa cikin aikin soji kuma aka tura shi yaƙi a Ukraine, inda ya rasa ransa.”

Ya ce yanzu haka ana shirye-shiryen mayar da gawar ɗalibin gida daga Rasha.

Ya ƙara da cewa “ina tattaunawa da iyalan mamacin, kuma zan ci gaba da tattaunawa da su domin bayyana masu duk bayanin da muka samu game da mutuwar ɗan’uwan nasu.”

Ba a dai san yadda aka yi Nyirenda ya fito daga gidan yari ba, amma Rasha ta rinƙa yi wa fursunoni tayin sakin su idan suka amince za su fafata a faɗan da take yi da Ukraine.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp