Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, ya yi gargadin cewa yakin da Rasha ke yi a Ukraine ka iya janyo abin da ya kira mummunar yunwa da kuma karancin abinci a duniya baki daya.
Ya ce, yawancin kasashen Afirka da kuma kasashe matalauta sun dogara kacokam a kan alkamar da Rasha da Ukraine ke samarwa.
Ya ce, ”abinci da man fetur da kuma takin zamani duk farashinsu ya yi tashin gwauron zabo, sannan karancin kudade da kuma jinkiri wajen shigar da kaya ko fitar da su duk matsala ce.”
Ya ce, duk wadannan ka iya jefa kasashe matalauta cikin garari.
Wadannan kasashe sun hada da Burkina Faso da Somalia da kuma Yemen wadanda tuni suke fadi-tashin yadda zasu ciyar da al’ummarsu.
Mr Guterres, ya yi kiran da a gaggauta tsagaita wuta domin guje wa fadawa matsalar karancin abinci a duniya.