Shugaban Rukunin kamfanin Dangote, Aliko Dangote, ya shaida wa gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari da ta hana fitar da masara zuwa kasashen waje, domin tabbatar da samar da abinci a kasar a yakin Rasha da Ukraine.
Dangote ya yi wannan kiran ne a yayin taron shugabannin masana’antu da sarrafa abinci na Najeriya karo na 4 a ranar Alhamis a Legas.
Gidauniyar Aliko Dangote, Bill & Melinda Gates Foundation (BMGF), da TechnoServe ne suka shirya taron, a karkashin shirin karfafa masu sarrafa abinci na Afirka (SAPFF).
Shirin na da nufin magance kalubalen da ke dadewa a fannin kayyade abinci ta hanyar amfani da tsarin da ya shafi kasuwa don taimakawa sama da masu sarrafa abinci 90 don kara karfinsu na samarwa da sayar da kayayakin abinci ga kasuwannin cikin gida.
Dangote ya bayyana cewa yakin Rasha da Ukraine zai haifar da karancin abinci, sakamakon rashin samun taki. A cewarsa, za a ga irin tasirin da yakin ke haifarwa a samar da abinci nan da watanni biyu ko uku masu zuwa a Najeriya.
Ya ce Rasha da Ukraine ne na daya da biyar a fannin noman alkama, wanda ya kai kashi daya bisa uku na noman alkama a duniya.