Majalisar Dinkin Duniya ta ce kusan mutum dubu 900 ne suka fice daga Ukraine, tun bayan da Rasha ta ƙaddamar da mamayar kasar, ranar Alhamis da ta gabata.
Sama da rabin adadin sun shiga Poland, yayin da wasu dubu 100 ɗaya suka nufi yamma zuwa kasar Hungary.
Hukumar kula da ƴan gudun hijira ta majalisar na turakarin ma’aikata da kayan agaji domin tallafa wa ‘yan gudun hijirar, da kuma makwabtan Ukraine wadanda suke bayar da mafaka ga mutanen.
Majalisar na rokon kusan dala miliyan dubu biyu domin gudanar da ayyukanta na jin-kai.
Hasashen da aka yi da farko cewa kusan ‘yan Ukraine miliyan hudu za su tsere daga kasar, alkaluman ka iya zarta haka matuka gaya.