Dakarun Rasha na ƙoƙarin yi wa birnin Kyiv kawanya, a lokacin da suka zafafa kai hare-hare a zagayen birnin.
Kamfanin labarai na Reuters ya ruwaito gwamnan Kyiv da na yankin Donetsk na cewa, hare-hare sun tsananta a wuraren da ake sa ran za a tsagaita wuta, domin bai wa fararen hula damar tserewa.
Tuni aka tsara cewa Rasha za ta tsagaita wuta a garuruwan da suke hannunta, ciki har da Mariupol da ke Donetsk.
“Jirgin dakon kaya yana kan hanyar zuwa Mariupol yanzu, za mu ba ku bayanin abin da ke faruwa…Lamarin ba mai sauƙi ba ne, ana ta ci gaba da luguden wuta,” in ji Gwamnan Donetsk Pavlo Kyrylenko cikin hirarsa da wata kafar labarai ta Ukraine.