Shugaban Masu Rinjye a Majalisar Wakilan Najeriya Alhassan Ado Doguwa ya isa ƙasar Romania tare da Shugaban Kwamatin Harkokin Waje Yusuf Buba a yunƙurin kwashe ‘yan ƙasar da suka nemi mafaka daga yaƙin Ukraine.
Wakilan sun je a madadin majalisar bayan ta zartar da wani ƙudiri da ya buƙaci su yi aiki tare da ɓangaren gwamnati don tabbatar da an kwaso ‘yan ƙasar kusan 5,000 da ke Poland da Romania da Hungary.
Ministan Harkokin Waje Geoffrey Onyeama ya ce ya yi magana da takwaransa na Hungary yana nema wa jirgin Najeriya izinin sauka don fara aikin.
A jiya Laraba Shugaba Muhammadu Buhari ya amince a kashe dala miliyan takwas da rabi – kusan naira biliyan uku da rabi – yayin aikin.
Lamarin na zuwa ne yayin da baƙaƙen fata ke kokawa kan wariyar launin fata da ake nuna musu a lokacin da suke neman ficewa daga Ukraine ɗin, inda wasu suka shafe kwanaki a kan layi saboda launin fatarsu.