fidelitybank

Yaki: Tinubu ya umarci Ministan tsaro da Hafsoshin soji su tare a Sokoto

Date:

Gwamnatin tarayya ta umurci karamin ministan tsaro, Bello Matawalle da sauran hafsoshin soji da su koma jihar Sokoto domin kawar da yankin Arewa maso Yamma daga barazanar ‘yan fashi da garkuwa da mutane da kuma ta’addanci.

Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na ma’aikatar tsaro, Henshaw Ogubike ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Gwamnatin ta ce wannan umarnin wani bangare ne na kara kaimi wajen kawar da yankin Arewa maso Yamma daga matsalolin ‘yan fashi da garkuwa da mutane da kuma ta’addanci.

Gwamnatin tarayya ta bayyana bakin cikinta dangane da ayyukan ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga a jahohi da kewaye, inda ta bayyana cewa wannan dabarar da ta dauka ya nuna jajircewar gwamnati na maido da zaman lafiya da tsaro a yankin.

A cewar sanarwar, yayin da suke yankin Arewa maso Yamma, za su sa ido kan yadda ake gudanar da ayyuka tare da tabbatar da cewa an fatattaki Bello Turji da ‘yan bindigar sa.

“Wadannan ’yan fashin sun rika yada bidiyon wata mota kirar sulke ta sojojin Najeriya da ta makale a wani wuri mai cike da ruwa.

“Kuma da daddare aka bukaci jami’an da su janye don gudun kada ‘yan bindiga su yi musu kwanton bauna, daga baya cikin dare ‘yan fashin suka je wurin, inda suka dauki hoton motar sulke da ta makale suna murna.

“Wannan lamari ya faru ne a kwashabawa, karamar hukumar Zurmi a Zamfara.

“Wannan ba abu ne da za a amince da shi ba, kasancewar shugaban kasa Bola Tinubu yana bayar da gagarumin goyon baya ga rundunar sojojin Nijeriya.

“Gwamnatin tarayya ta damu matuka game da barazanar ‘yan bindiga da ta’addanci a yankin Arewa maso Yamma.

“Saboda haka a shirye muke mu tura dukkan kadarorin da suka wajaba don tabbatar da cewa an kawar da wadannan masu aikata laifuka tare da dawo da zaman lafiya a cikin al’ummominmu,” in ji sanarwar.

Gwamnatin ta ce akwai bukatar a gaggauta daukar matakin yakar ‘yan ta’addar domin baiwa jama’a damar tafiya cikin walwala.

Sannan kuma ta tabbatar wa al’ummar jihohin Sakkwato da Katsina da Zamfara da Kebbi da ma daukacin yankin Arewa maso Yamma cewa jami’an tsaro ba za su bari a fatattaki ‘yan bindigar ba.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp