fidelitybank

Yajin aikin ma’aikatan NIMET ya hana wasu jirage tashi a Najeriya

Date:

Harkokin sufurin jiragen sama na fuskantar cikas a filayen tashi da saukar jiragen sama na cikin gida yayin da ma’aikatan hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ke gudanar da yajin aikin kan rashin ingancin yanayin aiki.

Yajin aikin da ya yi kwana biyu yana gudana ya haifar da maƙalewar fasinjoji a filin jirgin saman Nnamdi Azikwe da ke Abuja, da filin jirgin Murtala Muhammed da ke Legas da sauran filayen jiragen sama da ke faɗin ƙasar.

Kamfanin sufurin jiragen sama mafi girma a Najeriya, Air Peace ya sanar da dakatar da ayyukansa sakamakon yajin aikin.

Kamfanin ya sanar da cewa ya yanke shawarar dakatar da sufurin jiragensa ne saboda kiyaye rayukan fasinjojinsa.

Kafar yaɗa labarai ta Channels ta rawaito cewa a filin jirgin saman Legas, kamfanin XEJET da Aero Contractors, da Ibom Air sun yi aiki kamar yadda aka tsara a ranar Laraba, yayin da Air Peace bai yi aiki ba.

Domin shawo kan lamarin, ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya shirya ganawa da wakilan mambobin ƙungiyar ma’akatan hukumar NiMet masu zanga-zangar.

An shirya gudanar da taron a yau (Alhamis).

Ma’aikatan NiMet sun rufe cibiyoyin kula da yanayi a filayen tashi da saukar jiragen sama kuma sun janye duk ayyukan kula yanayi a faɗin ƙasar a ranar Laraba yayin da suke neman a biya musu buƙatunsu

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp