An tashi baran-baran a tattaunawa tsakanin ministan ilimi Adamu Adamu da shugabannin ɗalibai a Najeriya kan batun yajin aikin ƙungiyar malaman jami’a ta ASUU a Abuja.
Ɗaliban sun zargi ministan ilimi da ficewa zauren tattaunawar bayan sun gabatar da ƙorafinsu.
A lokacin da yake jawabi, shugaban ƙungiyar ɗaliban na Najeriya Sunday Ashefon ya faɗa wa ministan cewa ya kai ɗansa ƙasar waje karatu.
Bidiyo ya nuna yadda shugaban yake jawabi da kuma yadda ministan ya bayar da amsa da ficewa daga zauren tattaunawar.
“Mun gani a kafofin sada zumunta, kana biki ɗanka ya kammala karatu a ƙasar waje.yayenmu ba su da kudin kai mu ƙasahen waje, muna son a ware kuɗi domin ci gaban ilimi a ƙasar nan, mai girma minista muna son mu koma makaranta,” kamar yadda shugaban ɗaliban ya shaida wa Adamu Adamu.
Ministan ya ce, “abu ɗaya” da ya karba a tattaunawar shi ne batun shigar ɗalibai a tattaunawa da malaman jami’a, daga nan ya fice ya bar ɗaliban a wurin tattaunawar.
Yajin aikin na gargadi da malaman jami’a suka shiga suna neman gwamnati ta aiwatar da yarjejeniyar da suka kulla a 2009 kan ƙarin kuɗaɗen da ake kashewa ɓangaren ilimi.