fidelitybank

Yajin aikin ASUU: An ta shi babu dadi tsakanin ministan ilimi da shugabannin dalibai

Date:

An tashi baran-baran a tattaunawa tsakanin ministan ilimi Adamu Adamu da shugabannin ɗalibai a Najeriya kan batun yajin aikin ƙungiyar malaman jami’a ta ASUU a Abuja.

Ɗaliban sun zargi ministan ilimi da ficewa zauren tattaunawar bayan sun gabatar da ƙorafinsu.

A lokacin da yake jawabi, shugaban ƙungiyar ɗaliban na Najeriya Sunday Ashefon ya faɗa wa ministan cewa ya kai ɗansa ƙasar waje karatu.

Bidiyo ya nuna yadda shugaban yake jawabi da kuma yadda ministan ya bayar da amsa da ficewa daga zauren tattaunawar.

“Mun gani a kafofin sada zumunta, kana biki ɗanka ya kammala karatu a ƙasar waje.yayenmu ba su da kudin kai mu ƙasahen waje, muna son a ware kuɗi domin ci gaban ilimi a ƙasar nan, mai girma minista muna son mu koma makaranta,” kamar yadda shugaban ɗaliban ya shaida wa Adamu Adamu.

Ministan ya ce, “abu ɗaya” da ya karba a tattaunawar shi ne batun shigar ɗalibai a tattaunawa da malaman jami’a, daga nan ya fice ya bar ɗaliban a wurin tattaunawar.

Yajin aikin na gargadi da malaman jami’a suka shiga suna neman gwamnati ta aiwatar da yarjejeniyar da suka kulla a 2009 kan ƙarin kuɗaɗen da ake kashewa ɓangaren ilimi.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp