Kusan watanni 3 ke nan da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta fara yajin aikin bayan tabarbarewar yarjejeniyar da ta kulla da gwamnatin tarayya a shekarar 2021.
Daliban Najeriya da aka tilastawa zama a gida a lokacin karatu, sun fara bayyana damuwarsu kan yajin aikin da aka dade ana yi, tare da gudanar da zanga-zanga ta layi da kuma ta yanar gizo.
Zanga-zangar dalibai a Jami’ar Benin (UNIBEN) da Jami’ar Ambrose Alli da ke Ekpoma, dukkansu a jihar Edo a ranar Larabar da ta gabata, ta shiga wani yunkuri na intanet mai suna #EndASUUStrike.