fidelitybank

Yahudawa sun kashe yara 2,300 – Jakadan Falasdinawa a Najeriya

Date:

Jakadan Falasdinawa a Najeriya, ya yi ikirarin cewa hare-haren da Isra’ila ta kaddamar a kan Zirin Gaza tun bayan harin da Hamas ta kai wa kasar, sun yi sanadin mutuwar kananan yara fiye 2,300.

A cewar Abdullah Abu Shawesh, hare-haren sun kuma yi sanadin hallaka mata kusan 1,500.

Isra’ila dai ta lashi takobin wargaza kungiyar Hamas, wadda ta kai mummunan harin bazata, da ya yi sanadin kashe mutuwar mutum 1,400 tare da sace fiye da wasu 200.

Jakadan al’ummar Falasdinawan na wannan bayani ne yayin wani taron manema labarai da ya kira don sanar da duniya halin da ake ciki game da rikicin Isra’ila da Gaza da kuma yadda lamarin ya ranar Talata a Abuja, babban birnin Najeriya.

Abu Shawesh ya ce jimillar Falasdinawan da aka kashe tun daga ranar 7 ga watan Oktoba, sun kai 5791.

Jakadan ya kuma zargi kasashen Turai da mara baya ga Isra’ila kan abin da ya kira kisan kiyashin da take yi a yankunan Falasdin ba.

A cewarsa bai kamata a rika zaben dokokin kasashen duniya da za a yi aiki da su ba, sannan a yi watsi da wasu.

Abdullah Abu Shawesh ya ce matakin soja, bai taba yin aiki ba a lokutan baya, don haka ba zai yi aiki ba ma a wannan lokaci.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp