Gwamna Yahaya Bello na Jihar Kogi a ranar Alhamis ya tarɓi Kalifan Tijjaniya Sheikh Ibrahim Niasse da kuma shugaban ƙungiyar a Najeriya Muhamnadu Sanusi yayin da ake gudanar da taron addu’o’i na neman zaman lafiya.
Kamfanin labarai na NAN ya rawaito yadda gwamnan ya tarɓi shugabannin tare da sauran malamai a taron da aka yi wa laƙabi da ‘hanyoyin rayuwa ta hanyar Sunnar Annabi’ da ke gudana a Lokoja babban birnin Kogi.
Taron wanda zai tara malamai daga ciki da wajen Najeriya, za a shafe kwana biyu daga 6 zuwa 8 ga watan Janairu ana gudanar da shi, inda za a gabatar da maƙaloli.
Za kuma a ziyarci marasa lafiya a asibitoci daban-daban tare da yin zikirin Juma’a da kuma liyafar cin abinci da sunan murnar samuwar Annabi Muhammadu – amincin Allah ya tabbata a gare shi.
Kazalika wani Khalifan na Tijjaniyya Sheikh Ali Arabi na halartar makamancin taron a Kano ƙarƙashin jagorancin Gwamna Umar Ganduje da Sarkin Kano Aminu Ado.